Connect with us

Labarai

Obi da Kwankwaso sun nemi a yi adalci kan kisan Danshagamu a Kano

Published

on

Peter Obi da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso sun yi Allah-wadai da kisan mai sharhi kan harkokin siyasa a Kano, Ibrahim Khalil Danshagamu, tare da neman a hukunta waɗanda suka aikata laifin.

A saƙonnin ta’aziyyarsu daban-daban, jagororin siyasar sun buƙaci gwamnatin Kano da hukumomin tsaro su gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Danshagamu ya rasu bayan an kai masa hari da makami mai kaifi a gidansa da ke unguwar Gaida, Ƙaramar Hukumar Kumbotso. Rundunar ’yan sandan Kano ta ce ta kama mutum biyu da ake zargi da hannu a kisan.

Peter Obi ya ce bambancin ra’ayi ko suka ba zai taɓa zama hujjar amfani da tashin hankali ba, yana mai jaddada muhimmancin kare ’yancin faɗar albarkacin baki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!