Connect with us

Labarai

INEC ta sanya ranar 9 ga Satumba domin zaɓen cike gurbi a Dawakin Kudu

Published

on

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC, ta sanya ranar Asabar, 19 ga Satumba, 2026 domin gudanar da zaɓen cike gurbi a mazabar Dawakin Kudu ta Jihar Kano.

Hukumar ta bayyana cewa za a kuma gudanar da irin zaɓen a mazabun Gombe/Kwami/Funakaye na Jihar Gombe da Sakwa da Disina a Bauchi da kuma Udu a Delta.

A cewar INEC, za a fara kaɗa ƙuri’a daga ƙarfe 8:30 na safe zuwa 2:30 na rana a rumfunan zaɓen da aka ware.

Zaɓukan na da nufin cike guraben da suka samu sakamakon rasuwa, murabus ko wasu dalilan da suka sa kujerun ’yan majalisar suka zama babu wakilai.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!