Connect with us

Labarai

PDP ta yi Allah-wadai bisa tsarewar da EFCC ta yi wa Tambuwal

Published

on

Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta yi Allah-wadai da kamawa tare  da tsare tsohon gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal,  lamarin da ta ce jam’iyyar APC ce ke neman jefa dimokuraɗiyyar Najeriya cikin ruɗani.

 

A wata sanarwa Sakataren yada labaran PDP na jihar, Hassan Sahabi Sanyinnawal ya fitar, ya ce wannan na cikin yunƙurin cin zarafi da murƙushe jam’iyyun adawa a ƙasar.

 

Ya ce kamen na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara ƙoƙarin samar da haɗakar jam’iyyun adawa a ƙasar domin fuskantar zaɓe mai zuwa, inda kamen ba zai hana komai ba wajen yunƙurin da suke yi na kawo sauyi ba.

 

Bayan kamun nasa dai hukumar ta  EFCC ta ce,  ta tsare tsohon gwamnan na jihar Sokoto Aminu Waziri Tambuwal, bisa zarginsa da almundahanar kuɗi, da Rahotonni suka tabbatar da cewar  sanatan ya isa ofishin hukumar ne da kansa domin amsa gayyatar da aika masa a ranar Litinin, sannan ta riƙe shi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!