Labarai
Rahoto: Mutane 79,323 sun rasu sakamakon harin ta’addanci a Najeriya

Wani sabon rahoto da cibiyar sa ido kan ‘yancin addini a Afirka wato Observatory for Religious Freedom in Africa ta fitar ya ce, mutane 79,323 ne suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ta’addanci a Najeriya tsakanin shekarar 2020 zuwa 2025.
Rahoton, wanda aka ƙaddamar a birnin Jos, ya kuma nuna cewa an yi garkuwa da fararen hula 34,773 a cikin wannan lokaci.
A cewar rahoton da Jaridar The Punch ta fitar, ana samun hare-hare bakwai a kowace rana, inda kuma kusan mutum 36 ke rasa rayukansu a kullum.
Rahoton ya ƙara da cewa fiye da mutane 42,000 daga cikin waɗanda aka kashe fararen hula ne marasa hannu a rikicin.
You must be logged in to post a comment Login