KannyWood
Rarara ya yi martani ga masu sukarsa da cewa shi ba ɗan Kano ba ne
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2023/03/RARA.jpg)
Mawakin nan Dauda Kahutu Rarara, ya yi martani ga masu sukarsa da cewa shi ba ɗan Kano ba ne.
A hirarsa da Freedom Radio ya bayyana dalilan da suka sanya aka fi ganin ya fi ɗaukar ɗumi a siyasar Kano.
Rarara ya kuma sake jaddada hasashensa na cewar Alhaji Nasiru Yusuf Gawuna ne zai lashe zaɓen Gwamnan Kano.
Ya ce, yanzu a siyasar Kano tuni Ganduje ya dame Kwankwaso ya shanye balantana Abba.
Haka kuma ya yi martani ga mawaƙan da suke ganin ba za su iya haɗa hanya da shi ba a siyasa.
Mawaƙin ya kuma yi fida bisa dalilan da suka raba shi da dan takarar gwamna a jam’iyyar ADP Sha’aban Ibrahim Sharaɗa.
Ku kalli cikakkiyar tattaunawar a nan ta hanyar danna alamar Play.
You must be logged in to post a comment Login