Labarai
Rikicin Boko Haram ya lalata fiye da makarantu 5,000- Gwamna Zulum

Gwamnan Borno, Babagana Zulum, ya ce rikicin Boko Haram ya lalata gine-ginen makarantu sama da dubu biyar a fadin jihar.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a Maiduguri yayin kaddamar da wasu ayyuka, inda ya ce a lokacin da rikicin ya yi kamari, kimanin yara miliyan 2.2 ne ba sa zuwa makaranta, yayin da kasa da 500,000 ke samun damar karatu.
Haka kuma Gwamna Zulum, ya ce, gwamnatinsa ta kashe sama da naira biliyan 46.9 wajen inganta ilimin firamare da sakandare tsakanin shekarun kasafin kuɗi na 2025 da 2026.
You must be logged in to post a comment Login