Labarai
Iraƙi ta sake buɗe wasu hanyoyi uku a kan iyakarta da Iran

Iraƙi ta sanar da sake buɗe wasu hanyoyi uku a kan iyakarta da Iran, bayan da aka rufe su sakamakon wani harin jirgi mara matuƙi da aka kai kan bututun jigilar man fetur na Saudiyya.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ce mashigar Al-Shayb da ke lardin Maysan, wadda ake kira Chazaba a Iran, za ta koma karɓar fasinjoji daga yammacin jiya Lahadi.
Haka kuma, za a sake buɗe mashigar Shalamcha da ke lardin Basra.
A mashigar Mandali da ke lardin Diyala, za a dawo da harkokin kasuwanci daga ranar Talata.
You must be logged in to post a comment Login