Labarai
’Yan Sanda sun kama mutane 5 kan zargin sayar da jabun magunguna

Rundunar ’Yan Sanda ta kasa shiyya ta ɗaya da ke nan Kano ta kama mutane biyar bisa zargin sayar da jabun magungunan gargajiya da kuma yin sojan gona da sunan wani mai maganin gargajiya.
Wannan na cikin sanarwar da Kakakin Rundunar, DSP Abdullahi Hussaini, ya fitar a ranar Alhamis,
Rundunar ta bayyana cewa, ta kama mutanen ne bayan Dr. Abdulwahab Abubakar Goni Bauchi ya kai ƙorafi, yana zargin wasu da amfani da sunansa, kasuwancinsa da darussansa wajen tallatawa da sayar da jabun magunguna.
Waɗanda aka kama su ne Muhammad Usman, Husaini Kabir, Hassan Kabir, Suleiman Salihu da Nura Garba.
Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike domin gano tare da kama sauran waɗanda ake zargin suna da hannu.
Rundunar ta kuma shawarci jama’a su tabbatar da sahihancin magunguna, masu sayar da su da hanyoyin biyan kuɗi kafin yin ciniki, musamman a kafafen sada zumunta.
You must be logged in to post a comment Login