Connect with us

Labarai

Rundunar Yan sandan Bauchi ta kama mutane 2 da ke bai wa masu garkuwa da mutane bayanai

Published

on

Rundunar ‘Yan sandan Jihar Bauchi sun kama mutane 2 da ake zargi da bai wa masu garkuwa da mutane bayanai dangane da harin da aka kai a Karamar Hukumar Alkaleri.

 

Wannan na cikin sanarwar da mai magana da yawun rundunar yan Sandan, SP Nafiu Habib, ya fitar a Litinin din makon nan.

 

Ya ce harin ya faru ne a ranar 31 ga Yuli, 2026 a kauyen Gwanar Dutse da ke Gundumar Gwana a Karamar Hukumar Alkaleri, inda wani mutum mai shekara 46 ya samu raunin harbin bindiga a cinyarsa ta dama yayin ƙoƙarin tserewa.

 

Sanarwar ta ce, jami’an ‘yan sanda na Gobirawo sun kama waɗanda ake zargin.

 

Ya ce, binciken farko ya nuna cewa sun amsa zargin ba maharan bayanai, sannan an miƙa su zuwa Sashen Binciken Laifuka na Jihar Bauchi domin ci gaba da bincike kafin gurfanar da su a kotu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!