Connect with us

Labarai

Yan Sandan Sokoto sun cafke mutane 6 da ake zargi da fasa gidaje da sata

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Sokoto, ta ce, ta kama mutum shida da ake zargi da hannu a laifukan fasa gidaje, sata da kuma karɓar kayayyakin sata a wasu samame da ta gudanar bisa bayanan sirri.

 

Rundunar ta ce ta kuma ƙwato babura biyu da aka sace, sai keken ɗinki da kuma wayoyin salula da dama.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Ahmad Rufa’i, ya ce binciken ya biyo bayan rahoton fasa wani gida a unguwar Rumbukawa, inda aka sace keken ɗinki, wayoyi 13 da kuɗade.

 

A wani samame na daban kuma, rundunar ta ce ta kama wasu mutum uku kan zargin satar babura uku a unguwar Alkammawa, inda ta ƙwato biyu daga cikinsu.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Hassan Shaffa, ya ce rundunar za ta ci gaba da bin duk masu hannu a ayyukan laifi tare da ƙarfafa al’umma su rika bai wa jami’an tsaro bayanan sirri.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!