Labarai
Shugabannin PDP sun nemi Jonathan ya nesanta kansa da kalaman yan tsagin Turaki

Shugabannin jam’iyyar PDP na jihohi masu goyon bayan Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, sun buƙaci tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya fito ya nesanta kansa daga abin da suka kira amfani da sunansa da tsagin Kabiru Turaki ke yi.
Da ya ke magana a Abuja, jagoran shugabannin PDP na jihohi, Austin Nwachukwu, ya ce amfani da sunan Jonathan na iya yin illa ga martabarsa da ta jam’iyyar. Ya kuma yi zargin cewa tsagin na Turaki ba shi ne halastaccen shugabancin PDP ba, tare da kira ga jam’iyyar ta ɗauki matakan shari’a kan lamarin.
Jam’iyyar PDP bangaren Turaki ta ayyana Jonathan a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na PDP a zaɓen 2027, duk da cewa tsohon shugaban bai halarci taron da aka yi a Abuja ba, kuma har yanzu bai yi wata sanarwa a bainar jama’a kan batun ba.
You must be logged in to post a comment Login