Connect with us

Tsaro

Amurka ta  bukaci Ma’aikatar Tsaron kasar ta yi bayani  kan hare-haren da Amurkan ta kai Najeriya

Published

on

Majalisar Dokokin Amurka ta  bukaci Ma’aikatar Tsaron kasar (Pentagon) ta yi bayani  kan hare-haren saman da Amurka ta kai a Najeriya a ranar 25 ga Disamba, 2025, tare da karin haske kan rawar sojin Amurka a kasar. 

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa a baya, shugaban Amurka, Donald Trump, ya sanar da cewa sojojin kasar sa sun kai hare-hare kan mayakan da ke da alaka da ISIS a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, abinda gwamnatin  Tarayya ta ce an yi aikin ne da izininta, kuma bai saba wa ikon kasar ba.

Sai dai a wata wasika da ‘yan majalisar suka aike karkashin jagorancin Sara Jacobs da Jason Crow, sun nemi karin bayani kan doka da aka yi amfani da ita wajen kai harin, hadin gwiwar da aka yi da hukumomin Najeriya, da kuma yiwuwar jikkata fararen hula.

‘Yan majalisar sun kuma nuna shakku kan ikirarin cewa hare-haren sun kai ga ‘yan ISIS, inda suka ce babu kwakkwarar hujja da ke nuna akwai karfin kungiyar a jihar Sokoto.

Rahotanni sun kuma nuna cewa wasu makamai masu linzami sun gaza kai hari yadda ya kamata, inda wasu suka fadi a gonaki da gidajen jama’a, lamarin da ya kara jawo damuwa kan yiwuwar janyo asarar rayuka.

Majalisar ta bukaci Pentagon ta yi bayani kan adadin hare-haren da aka kai, wadanda aka kashe ko suka jikkata, kudin da aka kashe, da kuma shirin Amurka na nan gaba a Najeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!