Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Sai masu hannu da shuni sun tallafa mana – SEMA

Published

on

Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar kano SEMA ta ce dole ne sai masu hannu da shuni sun shigo cikin hukumar don bada tallafi ga wadanda suka shiga cikin wani iftila’i.

Shugaban hukumar Kwamared Sale Aliyu Jili ne ya bayyana hakan ta cikin shirin Barka da Hantsi na nan tashar freedom rediyo wanda shirin ya mayar da hankali kan yadda ake samun yawaitar zaftarewar gidaje sakamakon ambaliyar ruwa.

Ya ce yanzu gwamnatoci bazasu iya daukar nauye nauyen wasu mutanen da suka tsinci kan su a halin wani ibtila’i duba da yadda aka samu tabarbarewar tattalin arziki.

Ya kara da cewa jinkirin da akke samu daga hukumar na da nasaba da yadda aka dorawa gwamnati nauyin kowanne abu a bangaren tallafi na kare ibtila’i.

Kwamred Jili yace daga farkon damunar bana zuwa yau an samu ambaliyar ruwa wanda ya tafi da gidaje da gonakin mutane akalla sama da dubu ashirin.

Kwamred Sale Aliyu Jili ya yi kira ga al’ummar jihar kano da su rika gyara magudanan ruwan su domin yin hakan daya ne daga cikin abubuwan da ke takaita barazanar ambaliyar ruwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!