Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Samar da wuraren kiwo zai taimaka wajen samar da ayyukan yi – Kungiya

Published

on

Kungiyar masu fataucin dabbobi da kayayyakin abinci ta kasa ta bayyana cewa idan har gwmanati za ta samar da wuraren kiwo kamar yadda ta yi ikirari zai taimaka gaya wajen samar da ayyukan yi ga jama’a.

Shugaban kungiyar Malam Muhammad Tahir ne ya bayyana haka ta cikin shirin barka da hantsi na nan freedom radio wanda yayi duba kan yadda ya kamata a kawo zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma.

Malam Muhammad Tahir ya ce samar da ruga da gwmanatin Kano ke kokarin yi lamari ne da zai taimaka wa makiyaya da manoma wajen kyautata sana’oinsu.

A cewar sa kungiyar masu sana’oin fataucin dabbobi da kayayyakin abinci suna taka rawa wajen samar da ayyukan yi ga al’ummar kasa.

Malam Muhammad Tahir ya ce kamata ya yi gwamnati sanya hannu a wannan bangare don bunkasa sanar a gida da kasashen waje.

Ya ce jihar Legas na amfani da dabbobi fiye da dubu guda a kasar nan ya yin da kuma kasahen waje ke son Najeriya ta dinga fita naman dabbobi zuwa ketare.

Amma ya kara da cewar,  ‘kasancewar na gida bai koshi ba ya za’a yi a fita da shi’

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!