Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Samar da ma’aikatar kula da dabbobi zai bunkasa tattalin arziki – kungiyar Miyetti Allah

Published

on

Kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah ta bukaci gwamnatin tarayya da ta samar da ma’aikatar da za ta rika kula da dabbobi a kasar nan wanda hakan zai basu damar bai wa kasar nan gudunmawa wajen farfado da tattalin arziki.

Sakataren kungiyar Alhaji Usman Ngelzarma ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai a yau Alhamis.

Ya ce, a kasashen yammacin Afrika sun samar da irin wadannan ma’aikatu wanda hakan ya taimaka musu wajen magance matsalolin da suke fuskanta.

Alhaji Usman ya kara da cewa, bangaren da ke kula da su karkashin ma’aikatar aikin noma ba zai iya basu damar shiga wajen magance matsalar da kasar nan ke fuskanta ba, saboda haka yanzu lokaci yayi da Najeriya za ta amfana daga bangaren kiwo.

Gina Ruga ta zamani zai magance matsalolin Fulani -Munir Ahmad Gwarzo

Cin zarafin Fulani makiyaya babu abinda zai janyo sai kara rura wutar rikici- Hassan Kukah

Shugaba Buhari ya ce ‘yan Najeriya su yi watsi da kiran dattawan Arewa kan dawowar Fulani

Cikin matsalolin da ya lissafo ya ce suna fuskantar satar dabbobi da yin garkuwa da mutane da rikicin makiyaya wanda ya sanya har yanzu basa samun damar kula da rumbunan adana kayayyakin su.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!