Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sanata Adamu Bulkachuwa, ya musanta zargin sanya baki a shari’o’in matarsa

Published

on

Tsohon wakilin shiyyar Bauchi ta Arewa a Majalisar Dattawa, Sanata Adamu Bulkachuwa, ya musanta fahimtar da aka yi masa ta cewa ya taka rawa a wasu hukunce-hukunce da matarsa, Zainab Adam Bulkacuwa ta yanke a lokacin ta na shugabar kotun daukaka kara, inda ya ce an yi wa kalamansa bahaguwar fassara a lokacin da ya alakanta aikin matarsa da majalisa.

Sanatan ya yi kalaman ne a zaman karshe na Majalisa ta 9, inda ya yi ikirarin cewa ya yi amfani da matsayinsa wajen nema wa abokansa ’yan majalisa alfarma a wajen matarsa a lokacin da take rike da shugabancin Kotun Daukaka Kara.

A cewarsa, tsohon shugaban Majalisar Dattawa ne, Sanata Ahmed Lawal ya yanke masa hanzari inda ya rika yi masa katsalandan a lokacin da ya ke bayani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!