Labarai
Sanya Hijabi: Gwamnan Kwara ya sake rufe wasu makarantu
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2021/03/abdurrazak.png)
Gwamnatin jihar Kwara ta yi amai ta lashe kan matakin da ta ɗauka da farko na buɗe wasu makarantu waɗanda ta ba da umarnin rufewa a baya sakamakon saɓani kan ƙyale ƴaƴa mata su sanya hijabi.
A cewar babbar sakatariyar ma’aikatar ilimi ta jihar Kemi Adeosun, ta ce, yanzu an janye komawa makarantun da a baya aka amince su koma karatu a ranar Litinin.
Adeosun ta ce, wannan hukunci an zartar da shi ne da nufin zaman lafiya ga ɗaliban.
A cewar ta, Gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da gaskiya da girmama doka a kan kowane ɗan jihar.
You must be logged in to post a comment Login