Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Da ɗumi-ɗumi: Majalisar dokokin Kano ta buƙaci DSS su sanya ido kan Baffa Hotoro

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano, ta buƙaci gwamna Injiniya Abba Kabir Yusuf, da ya umarci hukumar tsaro ta DSS da rundunar ƴan sandan Kano su sanya ido a kan Malamin nan Baffa Hotoro tare da gurfanar da shi a gaban hukumar Hisbah da majalisar Malamai sakamakon kalaman ɓatanci da ya yi a kan mutanen garin Tudun Biri da harin jirgin sojin sama ya hallaka.

Majalisar ta ɗauki wannan mataki ne biyo bayan ƙudurin gaggawa da wakilin ƙaramar hukumar Ƙiru a zauren Usman Abubakar Tasi’u, ya gabatar yayin zaman majalisar na ranar Litinin.

Ɗan majalisar na Ƙiru, ya ce, kalaman da Baffa Hotoro ya furta ga mutanen da iftila’in ya ritsa da su sun yi muni matuka, don haka ya kamata a ɗauki mataki a kansa.

Bayan ganawa ta musamman da mambobin majalisar suka gabatar kan wannan batu ne suka amince baki ɗaya da zauren ya yi kira ga gwamnatin Kano da ta ɗauki waɗannan matakai guda huɗu a kan Malamin don gudun tada fitina.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!