Connect with us

Labarai

Shalkwatar tsaro ta musanta kai wa fararen hula hari ta sama a Neja

Published

on

Shalkwatar tsaron Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa fararen hula sun mutu a hari ta saman da sojoji suka kai a ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar Neja.

Shalkwatar ta kuma bayyana cewa, harin ya faru ne a sansanonin ‘yan bindiga ne kawai. 

 

A cewar daraktan yaɗa labaran ayyukan tsaro, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan.

Ya ce, an kai harin ne bayan samun bayanan sirri da suka nuna cewa, bayan taruwar ‘yan bindiga a ƙauyen Lukupe a ranar 9 ga Mayu, 2026.

 

Sojoji sun ce rundunar jiragen leƙen asiri ne suka kai hare-haren ta sama tsakanin karfe 11:59 na dare zuwa 6:00 na safe a wuraren da ake zargin maboyar ‘yan bindiga ne da suka haɗa da Katerma da Bokko da Kusasu da kuma Kuduru. 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!