Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Shekara daya kenan cif da rasuwar Abba Kyari

Published

on

An haifi tsohon shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Abba Kyari a garin Maiduguri da ke jihar Borno a ranar 23 ga watan Satumban 1953.

 

Ya kuma fara karatun boko a makarantar St. Paul College da ke Wusasa a Zari’a.

 

Abba Kyari ya samu digirinsa na farko kan nazarin zamantakewar dan adam a jami’ar Warwick da ke Ingila a 1980, kafin daga bisani ya kuma yin wani digiri din kan nazarin aikin lauya a jami’ar Cambridge a buraniyar.

 

Ya kuma halarci makarantar nazarin aikin lauya ta Najeriya 1983

 

Bugu da kari Abba Kyari ya kuma samu digiri na biyu akan harkar shari’ar a jami’ar Cambride a 1984.

 

Alakar-sa da shugaba Buhari ta fara ne a 1976 lokacin da Buharin ya ke rike da mukamin gwamnan mulkin soji na jihar Borno.

 

A watan Agustan shekarar 2015 ne kuma shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nadashi a matsayin mukamin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, mukamin da ya rike har zuwa lokacin mutuwar-sa a ranar 17 ga watan Afrilun 2020.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!