Labarai
Shufaba Tinubu ya buƙaci AU ta ɗauki mataki kan hare-haren ƙyamar baƙi a Afirka ta Kudu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci kungiyar Tarayyar Afirka AU ta ɗauki mataki kan abin da ya kira hare-haren ƙyamar baƙi da ake kai wa ‘yan Afirka da sauran ƙasashen duniya a Afirka ta Kudu.
Shugaban ya bayyana hakan ne a wani taron musamman na Tarayyar Afirka da aka gudanar a Luanda, babban birnin Angola, inda Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya wakilce shi.
Tinubu ya ce irin waɗannan hare-hare na barazana ga haɗin kan ƙasashen Afirka da zaman lafiya, don haka ya nemi a sanya batun cikin ajandar taron ƙoli na Tarayyar Afirka da za a gudanar a watan Janairun shekara mai zuwa, domin a tattauna tare da ɗaukar matakin da ya dace.
You must be logged in to post a comment Login