Labarai
Mai Martaba Sarkin Kano Sunusi II ya kammala Hawan Sallar Gani na farko

Mai Martaba Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu, ya kammala hawan Sallar Gani na kwanaki biyu da ya gudanar a sassa daban-daban na birnin Kano, domin nuna murnar bikin Maulidin fiyayyen halitta Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam.
Hawan Sallar Gani na bana ya gudana ne a matsayin wani bangare na bikin tunawa da ranar haihuwar Annabi Muhammad SAW, kuma an bayyana shi a matsayin karo na farko da aka gudanar da irin wannan hawa a tarihin Masarautar Kano.
A tsawon kwanaki biyun, Mai Martaba Sarkin ya kewaya sassa daban-daban na birnin Kano, inda ɗaruruwan manyan mutane da dubban al’umma, musamman matasa maza da mata, suka fito domin tarbar Sarkin da nuna farin cikinsu.
Wakilinmu na Masarautar Kano, Shamsu Dau Abdullahi, ya rawaito cewa yayin hawan, Mai Martaba Sarkin ya yi ta yi wa al’umma addu’o’in samun zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a jihar Kano da Najeriya baki ɗaya.
You must be logged in to post a comment Login