Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zambia ta yi watsi da tallafin kudi da Amurka ke shirin bata

Published

on

Gwamnatin kasar Zambia ta ce ba za ta amince da shirin taimakon kuɗaɗen tallafin lafiyar Amurka ba, wanda akai masa dabaibayi da wasu shariɗodin da suka kunshi ba su damar kai hannu a kan ma’adinan ƙasar ma su ɗimbin daraja. 

 

Ministan harkokin wajen Zambia Mulambo Haimbe ne ya tabbatar da hakan  da ya ce  Amurkar ta musu tayin dala biliyan biyu a matsayin tallafin kula da harkokin lafiya nan da shekaru biyar ma su zuwa.

 

Ministan ya kuma ce wani babban abin damuwa shi ne yadda Amurka ta gindaya yarjejeniyar kaiwa ga ma’adinan Zambia a matsayin ɗaya daga cikin shariɗoɗin bada tallafin kuɗaɗen.

 

Rahotanni sun ce ƙasashen Afirka da dama sun rattaɓa hannu a kan irin wannan yarjejeniya da Amurka, sai dai ƙasashen Ghana da Zimbabwe sun  yi watsi da ita.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!