Labarai
Shugaba Tinubu ya ta ya al’ummar Hausawa murnar ranar Hausa

Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, ya taya al’ummar Hausawa murna ta ranar Hausa, da ya ce manyan ginshiƙai ne da ke taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da haɗin kan kasar nan da ci gabanta.
Tinubu ya ce Babu shakka, harshen Hausa ya bunƙasa, ya kuma zama ɗaya daga cikin manyan harsunan haɗin kai da kasuwanci a sassa daban-daban na duniya.
A cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X, shugaban ya ce Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kai da ci gaban Najeriya
Shugaban ya taya al’ummar Hausawa murna bisa bikin Ranar Hausa, wanda ake gudanarwa a yau a fadar tarihi ta Daura, dake jihar Katsina.
You must be logged in to post a comment Login