Connect with us

Labarai

Yusuf Tuggar ya yi watsi da sakamakon zaben fidda gwani na gwamnan Bauchi

Published

on

Tsohon Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya yi watsi da sakamakon zaben fidda gwani na gwamnan APC a Jihar Bauchi, inda tsohon gwamna Mohammed Abubakar ya samu tikitin takarar jam’iyyar. 

 

Tuggar ya ce ya shiga zaben ne da fatan za a gudanar da sahihin zabe mai gaskiya da adalci wanda kowa zai amince da sakamakonsa.

 

Tuggar ya yi zargin cewa Ministan Lafiya, Ali Pate, ya taka rawa wajen kakaba wasu ‘yan takara a APC ta Bauchi. Ya kuma yi ikirarin cewa Pate ya gana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin rokon kada a ba shi damar zama dan takarar gwamna.

 

Ya kara da cewa irin wadannan matakai na rashin adalci ne ke haddasa ficewar wasu fitattun ‘yan siyasa daga APC. Tuggar ya bukaci Shugaba Tinubu da ya binciki lamarin tare da magance abin da ya kira rashin dimokuradiyya da ke gudana a jam’iyyar a jihar Bauchi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!