Connect with us

Labarai

Shugaba Tinubu zai jagoranci babban taro kan ma’adinai

Published

on

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, zai jagoranci wani babban taro kan ma’adinan da ake matuƙar buƙata a duniya, wanda za a gudanar a Manhattan, New York, ranar 21 ga Satumba 2026, a gefen taron Majalisar Ɗinkin Duniya.

 

Taron na Africa Minerals Strategy Group zai mayar da hankali ne kan yadda ƙasashen Afirka za su daina fitar da ma’adinansu a matsayin ɗanyen kaya kawai, su koma sarrafawa da ƙera kayayyaki a cikin nahiyar domin samun ƙarin darajar tattalin arziki. Afirka na da dumbin ma’adinai kamar lithium, copper, cobalt, graphite, manganese da rare earth elements.

 

Ana kuma sa ran shugabannin Afirka da masu zuba jari za su tattauna wani sabon tsarin haɗin gwiwa da zai taimaka wajen jawo jarin kuɗi, inganta sarrafa ma’adinai, samar da ababen more rayuwa da ƙarfafa matsayin Afirka a kasuwar ma’adinan duniya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!