Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Shugaban kasa ya yi afuwa ga wasu dattawa 3 a kasar nan

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi afuwa ga daya daga cikin dattawan kasar nan da suka yi fafutuka neman ‘yancin kai, marigayi, chief Anthony Enahoro da tsohon gwamnan tsohuwar jihar Bendel, Farfesa Ambrose Ali.

Ministan cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola ne ya bayyana haka, yayin wani taron manema labarai da safiyar yau a birnin tarayya Abuja; yana mai cewa, a yanzu mutanen an wankesu daidai suke da wadanda kotuna ba su taba kama su da laifi a kotuna ba.

A cewar ministan, akwai wasu fitattun al’ummar kasar nan guda uku wadanda suma suka suka ci gajiyar afuwar ta Shugaban kasa.

Haka zalika ministan na cikin gida ya kuma ce, shugaba Buhari, ya kuma ba da umarnin sakin wasu fursunoni guda saba’in a gidan gyaran hali da ke Kuje a birnin tarayya Abuja, a matsayin wani mataki na rage cunkoson da ke gidajen gyaran hali a kasar nan.

Ogbeni Rauf Aregbesola ya kara da cewa, daukar wannan matakin ya biyo bayan shawarar da kwamitin shugaban kasa kan rage cunkoso a gidajen yarin kasar nan ya bayar.

 

AI

 

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!