Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Sojojin Najeriya sun isa kasar Saudiya don gudanar da atisayen soja

Published

on

A jiya Talata, kakakin rundunar sojan kasar Masar ya bayar da sanarwar, sojojin ruwan kasar sun isa kasar Saudiyya, domin hadin gwiwa da takwarorinsu na kasashen Saudiyya, da Jordan, da Yemen, da Djibouti da kuma Sudan, wajen gudanar da atisayen soja.

Sanarwar ta ce, burin da ake neman cimmawa a wannan atisayen soja shi ne, inganta kwarewar sojojin wajen gudanar da yaki na hadin gwiwa a kan teku.

Rundunar sojojin Masar na kokarin bunkasa hulda da takwarorinta na kasashen da abin ya shafa, ta yadda za su tinkari kalubalen da suke fuskanta, da ma kiyaye tsaro da zaman lafiyar a shiyyar, kuma wannan atisayen soja wani mataki ne da aka dauka domin cimma wannan buri. A cikin kusan shekara daya da ta gabata, Masar ta hada kan kasashen Amurka, da Faransa, da Ingila, da Italiya, da hadaddiyar daular Larabawa, da Bahrain da kuma Kuwait, wajen gudanar da atisayen soja, atisayen da ya shafi rundunar sojin ta ta kasa da ruwa da kuma ta sama

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!