Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Addini

Sojojin Najeriya sun kashe kwamandojin Boko Haram 18 a jihar Borno

Published

on

Rundunar sojin kasar nan ta ce dakarunta da ke aikin samar da tsaro a yankin arewa maso gabashin kasar nan, sun kashe wasu kwamandojin kungiyar boko haram da ISWAP su goma sha takwas a jihar Borno.

 

A cewar rundunar cikin kwamandojin boko haram da sojojin suka kashe har da Bukar Gana Fitchmeram da akewa lakabi da Abu Aisha.

 

Mai magana da yawun rundunar burgediya janar Muhammed Yerima ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai.

 

Ya ce, ‘yan ta’addar sun fada komar dakarun sojin Najeriyar ne lokacin da suke kokarin kai wani harin ramuwar gayya a garin Damasak da ke jihar Borno.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!