Connect with us

Labarai

Sokoto: Yan Sanda sun hallaka ƴan bindiga biyu tare da ƙwato bindigu kirar AK 47

Published

on

Rundunar ’Yan Sandan jihar Sokoto ta ce, jami’anta sun hallaka ‘ƴan bindiga biyu tare da ƙwato bindigogi kirar AK 47 guda biyu daga wajensu bayan daƙile harin da suka yi yunƙurin kaiwa ƙauyen Dankadu da ke Ƙaramar Hukumar Illela.

 

Hakan  na cikin sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar, DSP Ahmad Rufa’i, ya fitar a baya baya nan.

 

Sanarwar ta kara dacewa  lamarin ya faru bayan samun kiran gaggawa cewa wasu ƴan bindiga sun fito daga dajin Tsauna domin kai hari ƙauyen Dankadu.

 

Rundunar ta ce, jami’an tsaro sun yi musayar wuta da ƴan bindigar, inda suka hallaka biyu daga cikinsu tare da ƙwato bindigun AK 47 guda biyu, da harsasai 54.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!