Labarai
Shugaba Tinubu da Atiku ba su halarci taron sanya hannu kan Yarjejeniyar zaman lafiya ba

‘Yan takarar shugabancin ƙasa da wasu jam’iyyun siyasa sun rattaba hannu kan Yarjejeniyar Zaman Lafiya ta Ƙasa domin gudanar da kamfen na zaɓen 2027 cikin lumana, tare da yin watsi da tashin hankali, kalaman ƙiyayya, yaɗa labaran ƙarya da tayar da zaune tsaye kan kabilanci ko addini.
Zaman ya gudana a birnin tarayya Abuja, a jiya Tallata ƙarƙashin jagorancin kwamitin zaman lafiya na ƙasa wato National Peace Committee (NPC) tare da haɗin gwiwar cibiyar Kukah , wato Kukah Centre, gabanin fara kamfen ɗin zaɓen 2027 a yau Laraba.
Sai dai wasu manyan ‘yan takarar shugaban ƙasa, ciki har da ɗan takarar APC, Shugaba Bola Tinubu, da ɗan takarar ADC, Atiku Abubakar, ba su halarci taron ba, inda Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ne ya wakilci Tinubu.
Daga cikin ‘yan takarar da suka halarta akwai Peter Obi na NDC, Adewole Adebayo na SDP da Omoyele Sowore na AAC.
Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya ce yarjejeniyar ta zo a daidai lokacin da ya dace, da ya bayyana cewa zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya zai gudana a 16 ga Janairu 2027, yayin da zaɓen gwamnoni da majalisun jihohi zai gudana a 6 ga Fabrairu 2027.
You must be logged in to post a comment Login