Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Ƙetare

Talabijin da Rediyo na Turkiyya ya ƙaddamar da sashensa na Hausa

Published

on

Ma'aikatan sashen Hausa na TRT

Kafar yada labaran ƙasar Turkiyya TRT ta ƙaddamar da sabbin sassan yaɗa huɗu da za su rinka yada shirye-shiryensu a harsuna daban-daban.

Sabbin bangarorin sun haɗar da sashen Hausa da Swahili da Ingilishi da kuma Faransanci, sun kuma fara aiki Juma’ar nan.

Darakta janar na TRT Mehmet Zahid Sobaci, ya ce za su mayar da hankali wajen yada shirye-shiryen da suka shafi nahiyar Afirka, a don haka ne suka ɗauki ma’aikata daga kasashe goma sha biyar na nahiyar.

Labarai masu alaƙa:

 Turkiyya ta ɗebe ma’aikata 9 daga BBC Hausa

Wannan dai na cikin gagarumin shirin da Gidan Talabijin da Rediyo na Turkiya ya gudanar inda zai mayar da hankali kacokan kan nahiyar Africa, musamman masu amfani da harshen Hausa.

Gidan Talabijin da Rediyo na Turkiyya ya ɗauki ƙwararren mai kula da shafin BBC Hausa Nasidi Adamu Yahaya a matsayin shugaban sashen Hausa na Turkiyya.

Ya kuma ɗaukar masa ƙwararrun mataimaka biyu da suka hada da Halima Umar Saleh wadda fitacciyar mai gabatar da shirye-shiryen intanet irinsu “Zamantakewa” da kuma Ishaq Khalid ƙwararren mai rahoton BBC cikin harsunan Hausa da Turanci.

Wasu ma’aikatan Rediyo da Talabijin ta Turkiyya

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!