Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yara dubu 33 a Katsina za su koyi karatu ta rediyo da talabijin – Bankin Duniya 

Published

on

Gwamnatin Jihar katsina ta ce, akalla yara dubu talatin da uku ‘yan firamare da ke aji daya zuwa uku za su koyi karatu ta kafar talabijin da rediyo karklashin shirin da bankin duniya ya dauki nauyi.

Shugaban shirin na Arewacin kasar nan Umar Bello ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da manema labarai jiya a jihar ta Katsina.

Ya ce duk da shirin koyarwar an zabi wasu daga cikin gidajen talabijin da rediyo ne amma duk da haka yaran sun fahimnci yadda ake furta kalmomi da kuma yin karatu na hausa da turanci.

Umar Bello ta cikin jawabin nasa ya ce, sun tsara koyarwa ta daban ta hanyar tura malamai guda 15 cikin unguwanni wanda kuma kowanne malami zai koyar da dalibai goma ne kacal.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!