Connect with us

Labarai

Trump ya yaba wa shugaba Tinubu bisa yaƙi da ta’addanci

Published

on

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yaba wa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa matakan da ya ke ɗauka na yaƙi da ta’addanci da magance matsalolin tsaro da suka addabi Najeriya, musamman hare-haren da ke shafar Mutane da dama.

 

A cikin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaba Tinubu mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026, Trump ya bayyana cewa yana mutunta irin jagorancin da Shugaban Najeriya ke yi wajen tinkarar matsalolin da ƙasar ke fuskanta.

 

Ya kuma ce abin alfahari ne a gare shi ya tsaya tare da Najeriya a yaƙin da take yi da ‘yan ta’adda domin ganin ƙasar ta samu zaman lafiya da ci gaba.

Trump ya ƙara da cewa dangantakar da ke tsakanin Amurka da Najeriya ta ƙara ƙarfafa musamman a fannin tsaro, inda ƙasashen biyu ke ci gaba da haɗa kai wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan Najeriya.

 

A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, wasiƙar ta nuna irin goyon bayan da gwamnatin Amurka ke bai wa ƙoƙarin gwamnatin Tinubu na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar Najeriya ba tare da la’akari da bambancin addini ko yanki ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!