Labarai
Hisbah ta gargaɗi ɗalibai kan aikata baɗala da sunan murnar kammala karatu

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta yi gargaɗi ga ɗaliban da ke shirin kammala karatunsu na makarantun sakandare a cikin makon nan da su guji aikata baɗala ko gudanar da ayyukan da suka saɓa wa tarbiyya da sunan shagulgulan kammala karatu.
Hukumar ta kuma yi kira ga ɗaliban da su guji sanya launuka ko rubuce-rubuce a jikin kayan makarantarsu da ka iya tauye martabar makaranta ko kuma karya ƙa’idojin tarbiyya.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Dakta Mujahid Aminuddeen, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya aikewa Freedom Radio.
You must be logged in to post a comment Login