Labarai
TSARO: Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan Boko Haram

Shalkwatar tsaro ta kasa ta ce dakarun Operation wutar tabki na rundunar sojin kasar nan sun kashe ‘yan boko haram da ‘yan kungiyar ISWAP da dama a yankin tabkin Chadi.
Hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shalkwatar tsaro ta kasa manjo janar John Enenche ya fitar a Abuja.
Sanarwar ta ce jiragen yakin dakarun ne suka yi luguden wuta kan maboyar ‘yan ta’addar a kauyukan Tundun Wulgo da Tumbun Gini da ke daf da tabkin Chadi.
Haka zalika sanarwar ta kuma ce an kai harin ne a ranar Alhamis din da ta gabata.
You must be logged in to post a comment Login