Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

TSARO: Sojojin Najeriya sun kashe ‘yan Boko Haram

Published

on

Shalkwatar tsaro ta kasa ta ce dakarun Operation wutar tabki na rundunar sojin kasar nan sun kashe ‘yan boko haram da ‘yan kungiyar ISWAP da dama a yankin tabkin Chadi.

Hakan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shalkwatar tsaro ta kasa manjo janar John Enenche ya fitar a Abuja.

Sanarwar ta ce jiragen yakin dakarun ne suka yi luguden wuta kan maboyar ‘yan ta’addar a kauyukan Tundun Wulgo da Tumbun Gini da ke daf da tabkin Chadi.

Haka zalika sanarwar ta kuma ce an kai harin ne a ranar Alhamis din da ta gabata.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!