Labarai
Tsohon shugaban APC na Kebbi ya rasu a hannun ƴan bindiga

Rahotanni daga jihar Kebbi, sun tabbatar da cewar Tsohon shugaban jam’iyyar APC na Jihar , Alhaji Muhammadu Besse, ya rasu a hannun ’yan bindiga bayan sace shi da suka yi a farkon wannan watan.
Wani ɗan jarida mai bibiyar harkokin tsaro a Arewacin kasar nan Bakatsine ne, ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata.
A cewar Bakatsine, Besse wanda shi ne tsohon shugaban APC na ƙaramar hukumar Koko/Besse, ya rasu da kawo yanzu shi da wanda aka gani a bidiyon da aka ɗauka a dajin Birnin Gwari duk sun rasa rayukan su yayin da suke tsare a hannun ’yan bindiga.
You must be logged in to post a comment Login