Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

UEFA ta dage wasan karshe na Champions League daga Russia zuwa Faransa

Published

on

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar turai UEFA ta dage wasan karshe na maza na gasar cin kofin zakarun turai Champions League na shekarar 2021/2022 daga kasar Russia zuwa Faransa.

Hakan na zuwa ne bayan wani zama da masu ruwa da tsaki na hukumar suka gudanar a ranar Juma’a 24 ga Fabrairun 2022 da muke ciki.

UEFA ta ce dage wasan ya biyo bayan yadda matsalar tashin hankali ke ci gaba da wakana tsakanin Russia da Ukraine.

Wasan karshen dai an tsara gudanarwa a birnin Saint Petersburg, wanda kawo yanzu za a gudanar a filin Stade de France da ke kasar Faransa a ranar Asabar 28 ga Mayun 2022.

Zuwa yanzu dai ana ci gaba da musayar wuta tsakanin kasashen Russia da Ukraine da sakamakon haka ake ci gaba da dage wasanni da dama a kasashen biyu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!