Connect with us

Labarai

Uwa da yayanta 3 sun rasu sakamakon gini da ya fado musu a Zaria

Published

on

Wani ginin ƙasa ya rushe ya hallaka wata uwa mai yara uku, Malama Habiba Nuhu da ‘ya’yanta biyu tare da jikarta yayin da suke barci da safiyar Laraba a birnin Zaria, karamar hukumar Zaria ta Jihar Kaduna.

Wani ganau, Mallam Ahmed wanda ke daga cikin dangin marigayiyar ya shaida wa cewa lamarin ya faru ne tsakanin karfe 3:30 zuwa 4:00 na safiyar Laraba, lokacin da katangar gida na makwabta ya rushe ya fado kansu (marasa sa’a) inda suka rasu nan take.

Mallam Ibrahim ya bayyana sunayen yaran da jikarta da suka rasu da cewa: Hauwa’u Nuhu, Aina’u Nuhu da Za’uma Nuhu. Ana cewa mahaifinsu, Mallam Nuhu Dogara, an sallame shi daga asibiti inda aka garzaya da shi domin samun kulawar gaggawa kafin a gudanar da sallar jana’izar marasa sa’ar.

Ya danganta faruwar lamarin da yanayin lalacewar katangar gidan makwabtan da ba a kula da ita ba tsawon lokaci.

Sai dai wakilinmu Hassan Ibrahim ya ruwaito cewa an binne mamatan kamar yadda addinin Musulunci ya tanada a birnin Zaria ranar Laraba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!