Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Mahaifin Malam Albaniy Zaria ya rasu

Published

on

Mahaifin malamin nan Malam Albani Zariya ya rasu.

Mahaifin na sa mai suna Malam Adam Ɗanjuma ya rasu da asubahin ranar Laraba.

Ministan sadarwa na kasa Isah Ali Pantami wanda aminin marigayi Albanin Zariyan ne ya sanar da hakan ta shafinsa na Facebook.

Anyi jana’izar marigayin da safiyar Laraba, a gidansa da ke unguwar Muchiya a garin Zaria.

Kisan Malam Albaniy Zaria

A watan Fabrairu na shekarar 2014 ne wasu ƴan bindiga suka hallaka Malam Albani Zariya tare da matarsa da ɗansa.

Ƴan bindigar sun buɗe wa malamin da iyalansa wuta a kan hanyarsa ta komawa gida daga makaranta.

Nan take matarsa ta rasu, inda shi kuma da ɗan na sa aka garzaya da su asibitin Wusasa da ke Zariya.

A nan kuma Allah ya karɓi rayukansu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!