Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Wada Sagagi ya yi watsi da ƙaddamar da Kwamitin Kamfen ɗin PDP a Kano

Published

on

Shugaban jam’iyyar PDP na Kano Alhaji Shehu Wada Sagagi ya yi watsi da kwamitin yaƙin neman zaɓen jam’iyyar da aka ƙaddamar a Kano.

Hakan na cikin wata sanarwa da mashawarcin jam’iyyar kan harkokin shari’a Barista Isah Wangida ya fitar a ranar Lahadi.

Sanarwar ta nuna cewar, taron ƙaddamar da Dr. Adamu Yunusa Ɗangwani a matsayin shugaban kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar a Kano haramtacce ne.

Barrista Wangida ya kuma yi watsi da waɗanda suka bayyana kansu a matsayin kwamitin riƙon jam’iyyar, yana mai cewa hakan ya ci karo da hukuncin Kotu.

Labarai masu alaƙa:

Wada Sagagi ya nemi Shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa yayi murabus

Kano: Kotu ta karɓe takarar Sadiq Wali ta bai wa Muhammad Abacha

Ya ce, Shehu Wada Sagagi shi ne halattaccen shugaban PDP a Kano bisa hukuncin da Kotu ta yi.

Ko a baya-bayan nan Babbar Kotun tarayya ta tabbatar da ɗan takararmu Alhaji Mohammed Sani Abacha wanda haka ke nufin mu kaɗai ne shugabanni a cewarsa.

A ƙarshe ya ce tuni suka garzaya Kotu da ƙorafi kan wannan taro da aka yi ba bisa ƙa’ida ba.

Ya kuma kira ga ƴan jam’iyyar da su kwantar da hankalinsu su ci gaba da biyayya ga umarnin shugabanni.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!