Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Wasanni

Wasan kwallon kurket: NCF za ta kaddamar da sabon mai horas wa

Published

on

Hukumar wasan kwallon kurket ta Najeriya wato NCF ta shirya kaddamar da tsohon dan wasan kasar Sri Lanka Asanka Gurusinha a matsayin sabon mai horas da ‘yan wasan Najeriya a cikin kwanaki masu zuwa.

Gurusinha mai shekara 44 wanda kuma mamba ne da ya taimakawa kasar sa ta Sri Lanka wajen lashe gasar cin kofin duniya a wasan kwallon kurket na shekarar 1996, ana sa ran zuwansa Najeriya don gabatar dashi kan mukamin da hukumar tashi.

Bayan aikin kula da kungiyar wasan kwallon kurket ta kasa, Gurusinha zai kasance cikin masu bayar da horo ga kananan masu horaswa na cikin gida.

Shugaban hukumar ta NCF Yahaya Ukwanya, ya ce, an zabi Gurusinha ne duba da irin gogewar da yake da ita a fagen wasan kurket din don kawo wa Najeriya cigaba a wasanni masu zuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!