Connect with us

Labarai

Wasu yan-bindiga sun sace tsohon mai magana da yawun soji a Katsina

Published

on

Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun yi garkuwa da tsohon Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin Najeriya, Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, tare da matarsa a Jihar Katsina.

Wani rahoto da jaridar Daily Post ta wallafa ya nuna cewa lamarin ya faru ne a ranar Asabar a yankin Matazu yayin da tsohon jami’in sojan da matarsa ke tafiya zuwa birnin Katsina.

Maharan sun tare motarsu tare da tafiya da su zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Wata majiya ta tsaro ta bayyana cewa direban motar ya samu raunin harbin bindiga lokacin harin, amma ya yi nasarar tserewa.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Katsina da kuma rundunar sojoji ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!