Connect with us

Labarai

Katsina: Mutanen gari sun dakile yunkurin ‘yan bindiga na kai hari musu hari

Published

on

Mazauna garin Gurbi da ke karamar hukumar Kankara a jihar Katsina sun dakile yunkurin ‘yan bindiga na shiga garinsu domin kai hari.

 

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa maharan sun iso da yamma, amma jama’ar gari sun taru tare da tare hanyarsu, lamarin da ya hana su shiga cikin garin.

 

Rahotanni sun ce bayan da ‘yan bindigar suka kasa shiga garin ne kuma suka bude musu wuta tare da kashe sama da mutum 10 a yankin Nagodi. 

 

Majiyar ta kuma ce tun kafin harin sun sanar da jami’an tsaro bayan samun bayanan sirri, amma ba a samu dauki ba.

 

Har zuwa wannan lokacin, rundunar ‘yan sanda da ofishin kwamishinan tsaro na cikin gida na jihar Katsina ba su fitar da wata sanarwa ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!