Connect with us

Labarai

Wike ya musanta zargin jam’iyyar ADC na hana ta amfani da Eagle Square

Published

on

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya musanta zargin da jam’iyyar hadaka ta ADC ta yi cewa an hana ta amfani da dandalin Eagle Square.

 

Wike ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a Abuja yayin rangadin duba ayyukan gine-gine.

 

Ya ce zargin cewa an hana wasu jam’iyyu amfani da dandalin Eagle Square ba shi da tushe.

A cewarsa, babu wata buƙata a hukumance da jam’iyyar ADC ta gabatar da sunan tana son ta yi amafi da dandalin.

 

Ya jaddada cewa Eagle Square a buɗe yake ga dukkan jam’iyya da kungiyoyi matuƙar sun bi ka’ida kuma sun biya kudin da aka ƙayyade.

 

Sai dai jam’iyyar ADC ta dage cewa ta bi dukkan matakan da doka ta tanada, inda ta ce ta riga ta mika takardar buƙata domin neman amfani da dandalin. Jam’iyyar ta bayyana cewa zargin cewa ba a karɓi wata takarda daga gare ta ba ba gaskiya ba ne.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!