Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kasuwanci

Ya kamata matasa su dage wajen koyon dabarun kasuwancin zamani – NCC

Published

on

Shugaban hukumar sadarwa ta ƙasa NCC, Farfesa Umar Garba Ɗanbatta ya buƙaci matasan da aka bai wa horon dabarun kasuwancin zamani da su alkinta ilimin da suka samu ta hanyar da ta dace.

Farfesa Ɗanbatta ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi ga waɗanda suka samu kyautar kayayyakin gudanar da kasuwancin ta kafafen sadarwa bayan kammala horon.

“Ya kamata matasan mu su mayar da hankali wajen koyon ilimin kasuwancin zamani don ganin sun zamo masu dogaro da kansu,” in ji shi.

A nasa jawabin shugaban makarantar Digital Bridge Institute, Farfesa Muhammad Ajiya, ya ce an horar da matasa dabaru iri-iri har da na shugabanci da zai taimaka musu wajen cimma burinsu a rayuwa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!