Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Yajin aiki: An cimma matsaya tsakanin ƙungiyar NARD da gwamnatin tarayya

Published

on

Gwamnatin tarayya ta cimma matsaya da ƙungiyar likitoci masu neman ƙwarewa ta ƙasa NARD, kan batun janye yajin aikin da suka tsunduma makwanni biyu da suka gabata.

Rahotanni sun bayyana cewa, ma’aikatar lafiya ta ƙasa za ta biya su sama da naira biliyan 4 nan da mako ɗaya bayan cimma yarjejeniyar.

Sanarwar da ma’aikatar lafiyar ta fitar ta ce, gwamnatin za ta biya kuɗaɗen Ariya na likitocin da kuma aiwatar da kwaskarima ga mafi karancin alabashi da aka cimma yarjejeniya a watan Disambar 2019 kuma shugaban Buhari ya sanya hannu.

Matuƙar ba ku yi aiki ba, ba za mu biya ku albashi ba – Gwamnatin tarayya ga ƙungiyar NARD

a cewar sanarwar, tuni gwamnatin tarayya ta aika da sunayen Asibitoci 38, ga ofishin kasafin kuɗi don tantancewa tare da biyan su haƙƙokin su.

Kungiyar likitocin ta tsunduma yajin aikin sai baba ta gani a ranar 2 ga watan Agusta, sakamakon ƙin cika alƙawuran da ta zargi gwamnatin tarayya da yi akan matsayar da suka cimma a baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!