Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Yajin aiki : An tashi baram-baram a tattaunawa da kungiyar kwadago da gwamnati

Published

on

An tashi baram-baram bayan da aka kwashe awa 8 ana tattaunawa da gwamnatin tarayya da kungiyar kwadago ta kasa biyo bayan rashin cimma matsaya.

Wannan na dauke cikin sanarwar da mataimakin shugaban kungiyar kwadago ta ta kasa Ameachi Asugwani ya fitar cewa gwamnatin na son cimma kudoruri a taron amma ta kasa samar da mafuta wajen warwae matsalar

Ameachi Asugwani ya ce kungiyar kwadago na bukatar gwamnatin tarraya ta yi nazari kan karin kudin man fetur da wutar lantarki a kasar nan wanda ya sababa ta tashin gwauran zabi na kayayyakin masarufi a kasar nan

Sai dai a cewar gwamnatin taq yi karin ne saboda ta janye tallafin da take baiwa dilalan mai.

A dai ranar Litinin ne kungiyar kadago ta kasa ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki 7 ta janye karin firashin man ko kuma ta tsunduma yajin sai baba ta gani.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!