Connect with us

Labarai

Yan bindiga sun kai hari garin Adunu da ke jihar Neja

Published

on

Mazauna yankin Adunu da ke jihar Neja sun wayi gari cikin tashin hankali a safiyar yau 11 ga watan Mayu, bayan rahotannin cewa ƴan bindiga sun shiga garin Kwakuti wanda nan ne mahaifar ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar Paikoro da Bosso a jihar inda Mazauna yankin ke ci gaba da neman hanyar tsira ta hanyar barin Garuruwan nasu.


‎Rahotonni sun bayyana cewa ƴan bindigan sun shiga garin Adunu da ke yankin Kwakuti, lamarin da ya sa al’ummar yankin ke ci gaba da tserewa domin neman mafaka.

 

A halin yanzu, garin Kwakuti ya koma tamkar sansanin masu gudun hijira sakamakon yawaitar mutanen da ke arcewa daga yankunan da rikicin ya shafa.


‎An tabbatar da kashe mutum guda yayin da wasu suka suka jikkata.

 

Haka kuma al’ummar yankin na kira ga gwamnati da ta gaggauta turo jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!